Abubuwan da Trump zai tattauna da Buhari a Amurka



Shugaban Najeriya Muhammadu BuhariHakkin mallakar hotoGETTY IMAGES
Image captionA farkon watan Afrilu Trump ya gayyaci Buhari zuwa White House
Shugaban Najeriya Muhammadu Buhari ya nufi Amurka domin ganawa da shugaba Donald Trump wanda ya gayyace shi zuwa fadar White House.
Shugaba Buhari zai bar Najeriya zuwa Amurka a ranar Asabar.
Wata sanarwa da mai ba shugaban na Najeriya shawara kan harkokin yada labarai, Femi Adeshina ya fitar ta ce Buhari da Trump za su gana da juna a ranar Litinin tare da cin liyafar abinci a Fadar White House.
Ya ce shugabannin biyu za su tattauna kan batutuwan da suka shafi bunkasa tattalin arziki da yaki da ta'addanci da kuma ci gaban mulkin dimokradiyya a yammacin Afirka.
Shugaba Donald Trump ne dai ya gayyaci Buhari zuwa Amurka a farkon watan Afrilu.
Wannan ne karon farko da Shugaba Buhari zai gana da Donald Trump a fadarsa ta White House a Washington.
Sanarwar ta kuma ce, shugaba Buhari zai gana da wasu rukunin kamfanonin Amurka a bangaren aikin noma da kiwo da sufurin jiragen sama.
Shugaba Trump ya taba bayyana kasashen Afirka a matsayin "wulakantattu" a cikin watan Janairun da ya gabata, kafin daga bisani shugaban ya musanta.
Ana ganin a yanzu Mista Trump na kokarin inganta huldar Amurka ne da Najeriya, musamman ganin yadda China ke ci gaba da mamaya a Afrika.
A 2017, gwamnatin Trump ta amince ta sayar wa da Najeriya jiragen yaki goma sha biyu da wasu kayayyakin kula da sha'anin tsaro da darajarsu ta kai dala miliyan 600.
A baya, tsohuwar gwamnatin Obama ta ki amincewa da cinikin jiragen, saboda fargaba a kan wasu dalilai.
Wannan ne karo na biyu da shugabannin Amurka suke gayyatar shugaba Buhari Fadar White House.
A shekarar 2015, tsohon Shugaban Amurka Barack Obama ya taba gayyatar shugaban na Najeriya zuwa Washington.

Comments

Popular posts from this blog

CAUSES OF GREENHOUSE EFFECT

BEST OF MOHAMMED SALAH

Economic importance of Mangifera indica